FEC Ta Amince Da Ayyukan Jirgin Kasa Na Dala Biliyan 2.99 A Lagos, Kano Da Kaduna



Majalisar zartarwa ta tarayya (FEC) ta amince da kwangilolin ayyukan jirgin ƙasa guda uku da kudinsu ya kai dala biliyan 2.99 a jihohin Lagos, Kano da Kaduna.

Ministan kudi kuma mai kula da tattalin arziki, Taiwo Oyedele, ya bayyana hakan bayan taron mako-mako na majalisar da aka gudanar a Abuja. Ya ce matakin ya dace da shirin gwamnati na inganta ababen more rayuwa domin bunƙasa tattalin arziki da walwalar al’umma.

Ya kuma bayyana cewa an kafa wani kwamitin musamman kan bangaren wutar lantarki karkashin jagorancin Shugaba Bola Tinubu.

Oyedele ya ce ayyukan za su taimaka wajen inganta zirga-zirga a manyan birane tare da ƙarfafa harkokin kasuwanci.

Ya jaddada muhimmancin Lagos, Kano da Kaduna.

A cewarsa, layin jirgin ƙasa na Lagos zai tashi daga Marina zuwa yankin Lekki, yayin da na Kano da Kaduna za su rage cunkoso tare da tallafa wa kasuwanci a arewacin ƙasar.

More from this stream

Recomended