Falgore ya zama sabon kakakin majalisar dokokin jihar Kano

An zaɓi, Jibrin Isma’il Falgore wakilin karamar hukumar Roggo a majalisar dokokin jihar Kano a matsayin sabon kakakin majalisar.

Falgore mamba ne a jam’iyar NNPP dake da mafiya rinjaye mambobi a majalisar dokokin inda aka zabe shi ba tare da hamayya ba.

Dan majalisar mai wakiltar karamar hukumar Dala, Lawal Hussaini(NNPP)shi ne ya gabatar da s sunan Falgore ga yan majalisar a matsayin mai yin takarar shugaban majalisar inda kuma ya samu goyon mamba mai wakiltar karamar hukumar, Takai Musa Ali Kachako(APC).

Har ila yau an zaɓi, Muhammad Bello Butubutu wakilin karamar hukumar Rimin Gado a matsayin sabon mataimakin kakakin majalisar.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]