An zaÉ“i, Jibrin Isma’il Falgore wakilin karamar hukumar Roggo a majalisar dokokin jihar Kano a matsayin sabon kakakin majalisar.
Falgore mamba ne a jam’iyar NNPP dake da mafiya rinjaye mambobi a majalisar dokokin inda aka zabe shi ba tare da hamayya ba.
Dan majalisar mai wakiltar karamar hukumar Dala, Lawal Hussaini(NNPP)shi ne ya gabatar da s sunan Falgore ga yan majalisar a matsayin mai yin takarar shugaban majalisar inda kuma ya samu goyon mamba mai wakiltar karamar hukumar, Takai Musa Ali Kachako(APC).
Har ila yau an zaɓi, Muhammad Bello Butubutu wakilin karamar hukumar Rimin Gado a matsayin sabon mataimakin kakakin majalisar.