Falgore ya zama sabon kakakin majalisar dokokin jihar Kano

An zaÉ“i, Jibrin Isma’il Falgore wakilin karamar hukumar Roggo a majalisar dokokin jihar Kano a matsayin sabon kakakin majalisar.

Falgore mamba ne a jam’iyar NNPP dake da mafiya rinjaye mambobi a majalisar dokokin inda aka zabe shi ba tare da hamayya ba.

Dan majalisar mai wakiltar karamar hukumar Dala, Lawal Hussaini(NNPP)shi ne ya gabatar da s sunan Falgore ga yan majalisar a matsayin mai yin takarar shugaban majalisar inda kuma ya samu goyon mamba mai wakiltar karamar hukumar, Takai Musa Ali Kachako(APC).

Har ila yau an zaɓi, Muhammad Bello Butubutu wakilin karamar hukumar Rimin Gado a matsayin sabon mataimakin kakakin majalisar.

More News

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...