Falgore ya zama sabon kakakin majalisar dokokin jihar Kano

An zaɓi, Jibrin Isma’il Falgore wakilin karamar hukumar Roggo a majalisar dokokin jihar Kano a matsayin sabon kakakin majalisar.

Falgore mamba ne a jam’iyar NNPP dake da mafiya rinjaye mambobi a majalisar dokokin inda aka zabe shi ba tare da hamayya ba.

Dan majalisar mai wakiltar karamar hukumar Dala, Lawal Hussaini(NNPP)shi ne ya gabatar da s sunan Falgore ga yan majalisar a matsayin mai yin takarar shugaban majalisar inda kuma ya samu goyon mamba mai wakiltar karamar hukumar, Takai Musa Ali Kachako(APC).

Har ila yau an zaɓi, Muhammad Bello Butubutu wakilin karamar hukumar Rimin Gado a matsayin sabon mataimakin kakakin majalisar.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]