EFCC ta kama mutane 20 masu sayen kuri’a a zaben kananan hukumomin Abuja

Wakilan jam’iyyu da basu gaza 20 ba ne aka kama da aikata laifin sayen kuri’a ranar Asabar a wurin zaɓen ƙananan hukumomi 6 dake faɗin birnin tarayya.

Jami’an hukumar EFCC dake yaki da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta’annati ne su ka kama mutanen a ƙananan hukumomin Abaji, Kuje, Kwali da kuma Gwagwalada a yayin zaɓen da ya gudana.

Tuni dai hukumar zaɓe ta ƙasa mai zaman kanta INEC ta sanar da cewa jam’iyar APC ta lashe kujeru biyar a cikin ƙananan hukumomin 6 c yayin da PDP ta tashi da kujera guda.

Mai magana da yawun hukumar EFCC  Dele Oyewale ya ce biyu daga cikin mutanen an kama su ne a Abaji, 9 a Gwagwalada huɗu a Kuje a yayin da sauran huɗun aka kama su a Kwali.

Oyewale ya bayyana cewa an kama mutanen da kuɗaɗe masu yawa da su ka kai  sama da naira  miliyan 30 a dai-dai lokacin da suke kokarin sayen kuri’a a ya yin da ake cigaba da gudanar da bincike.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]