Dan Majalisar Sokoto Ya Fice Daga APC Zuwa ADC



Ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Illela/Gwadabawa a jihar Sokoto, Isah Ambarura, ya fice daga jam’iyyar APC zuwa ADC.

Mataimakin shugaban kwamitin dokoki da harkokin majalisa ya bayyana cewa ya ɗauki matakin ne bayan lura sosai, yana mai cewa sabon matsayinsa zai ƙara masa damar yi wa al’ummarsa hidima.

A wani ɓangaren kuma, Jakduwa Kaikuku daga jihar Yobe ya koma APC daga PDP.

Sauya sheƙar ‘yan majalisa na ci gaba da ƙaruwa a majalisar dokoki, yayin da ake tunkarar zaɓen shekarar 2027. A kwanakin baya, wasu ‘yan majalisa daga jihohin Kano, Yobe, Lagos, Kaduna da Kebbi sun sauya jam’iyyunsu zuwa jam’iyyu daban-daban.

More from this stream

Recomended