Dakarun Najeriya Sun Kuɓutar Da Ƴan Mata 12 Da Ƴan Ta’adda Suka Sace A Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta sun sami nasarar kuɓutar da wasu ƴan mata 12 da aka yi garkuwa da su a gundumar Mussa da ke cikin ƙaramar hukumar Askira/Uba a jihar Borno, bayan wasu mayaƙan ISWAP sun sace su.

A cikin sanarwar da rundunar ta fitar da yammacin Asabar, an bayyana cewa an maida ƴan matan zuwa wani sansanin soji da ake tsaro sosai domin duba lafiyarsu kafin a miƙa su ga iyalansu.

An sace su ne a ranar 23 ga Nuwamba, a lokacin da suke aikin gona a yankin, inda membobin ISWAP ke gudanar da ayyukansu.

Sojojin sun jinjina wa dakarunsu da sauran jami’an tsaro da suka bayar da gudunmawa wajen kubutar da ƴan matan.

Sanarwar ba ta bayyana yadda aka aiwatar da ceto matan dalla-dalla ba.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]