Buhari ya gana da gwamnonin APC

Shugaban kasa, Muhammad Buhari yayi wata ganawa da gwamnonin jam’iyar APC a fadar Aso Rock.

Babau wata sanarwa da aka fitar kan dalilin taron sai dai wata majiya ta bayyana cewa taron baya rasa nasaba da zaben mutumin da zai yi wa jam’iyar APC takarar mataimakin shugaban kasa.

Tun bayan kammala zaben fitar da gwani da ya bawa tsohon gwamnan jihar Lagos, Bola Ahmed Tinubu nasara ake ta kai ruwa rana musamman wajen ganin mutumin da ya dace ya yi masa mataimaki.

Wasu majiyoyi na kusa da Tinubu sun bayyana cewa hankalin sa yafi kwanciya da tsohon gwamnan jihar Borno, Kashim Shettima a matsayin mataimaki.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaĆ™i da yiwa tattalin arzikin Ć™asa ne ya hana shi bayyana...