Atiku Ya Soki Soke Rajistar Jam’iyyar NDC



Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya yi allawadai da hukuncin wata kotun tarayya da ke Lokoja a jihar Kogi wanda ya soke umarnin yi wa jam’iyyar NDC rajista.

Atiku, wanda ke ƙarƙashin jam’iyyar ADC, ya zargi gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da yunƙurin raunana jam’iyyun adawa domin ƙarfafa tsarin jam’iyya ɗaya a ƙasar nan.

Mai shari’a Isah Dashen ya ce an soke hukuncin ne saboda rashin shigar da jam’iyyar PMP cikin ƙarar duk da cewa tana da ruwa da tsaki a shari’ar.

A wata sanarwa da ofishin yaɗa labaran Atiku ya fitar, ya ce hana ‘yan ƙasa damar samun zaɓuɓɓukan siyasa na iya haddasa rikici da kuma barazana ga dimokuraɗiyya.

Ya kuma buƙaci ɓangaren shari’a su kare mutuncinsu tare da kauce wa siyasa domin ci gaba da kasancewa mafakar talakawa.

More from this stream

Recomended