Sanata Rufai Sani Hanga ya musanta rahotannin da ke cewa zai sauya sheƙa daga jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC) zuwa APC, inda ya ce har yanzu shi cikakken ɗan jam’iyyar NDC ne.
Da yake magana a wata tashar rediyo a Kano, Hanga ya ce bai taɓa shirya ficewa daga jam’iyyarsa ba.
Sai dai ya bayyana cewa a ganinsa NDC ba ta da ƙarfin da za ta kayar da APC a zaɓen shugaban ƙasa, ko da yake ya yi hasashen cewa jam’iyyar za ta yi nasara a Jihar Kano.
Hanga ya kuma ce har yanzu yana mutunta jagoran jam’iyyar, Rabiu Musa Kwankwaso.
Game da zaɓen ɗan takarar gwamna na NDC a Kano, Hanga ya bayyana cewa an taɓa sanar da shi cewa za a tsayar da Mustapha Kwankwaso takarar gwamna, kuma ya amince ya jagoranci kamfen ɗinsa. Daga baya kuma, Aminu Abdussalam Gwarzo ya tuntube shi tare da ba shi tayin ya zama mataimakinsa, wanda ya ce ya amince da shi duk da cewa yana kallon hakan a matsayin koma baya. Sai dai daga bisani ya ji cewa an zaɓi Mustapha Kwankwaso a matsayin mataimakin Gwarzo.
Hanga Ya Musanta Shirin Komawa APC, Ya Ce Har Yanzu Yana NDC

