APC ta lashe zaɓen dukkanin shugabannin ƙananan hukumomin jihar Ekiti

Jam’iyar APC ta lashe dukkanin zaɓen shugabannin kananan hukumomin jihar Ekiti da kuma na kujerun kansiloli 177 da aka gudanar.

A ranar Asabar ne hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Ekiti ta gudanar da zaɓe a dukkanin ƙananan hukumomin jihar.

A cewar kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN jami’an tattara sakamakon zaben sune suka gabatar da sakamakon a hedikwatar hukumar dake Ado-Ekiti.

A ranar Lahadi ne shugaban hukumar, Cornelius Akintayo ya yabawa masu kada kuri’a kan yadda aka gudanar da zaɓen lafiya.

More News

Sojan Jamhuriyar Nijar sun kama Gawurtaccen Ɗan Fashin dajin Najeriya Kachalla Mai Daji

Dakarun sojan Jamhuriyar Nijar sun samu nasara kama gawurtaccen ɗan fashin dajin nan mai suna Kachalla Mai Daji a garin Illela dake kan iyakar...

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraɗiyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...