APC ta lashe zaɓen duka kujerun shugabannin ƙananan hukumomi 27 na Jihar Borno

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) reshen jihar Borno, ta lashe dukkan kujerun shugabanni 27 da na kansiloli 312 a zaben kananan hukumomin jihar Borno da aka gudanar a ranar Asabar.

Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Jihar Borno, BOSIEC, Lawan Maina ne ya bayyana haka a lokacin da yake bayyana sakamakon zaben da aka gudanar ranar Lahadi a Maiduguri.

“Bayan gudanar da zaben a ranar Asabar, a yau mun samu sakamako daga kananan hukumomi 27 kuma kamar yadda doka ta ba mu a sashe na 10.”

A matsayina na babban jami’in zaben jihar, zan karanta sakamakon kamar haka:

“Jam’iyya mai mulki, APC ta lashe dukkan kujerun shugabannin kananan hukumomin jihar 27.”

Haka kuma, jam’iyya mai mulki ta lashe dukkan kansiloli (kansiloli) 312 a daukacin kananan hukumomin jihar.

“Da wannan ne muka kawo karshen wannan aikk kuma za a gabatar da takardar shaida ga wadanda suka yi nasara a wani lokaci da za a bayyana nan ba da jimawa ba,” in ji Maina.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...