An yi hasarar rayuka 6 a wani mummunan haɗarin mota a hanyar Kaduna zuwa Zaria

Rahotanni sun nuna mutane 6 sun mutu yayin da 11 suka samu raunuka a wani hatsarin mota da ya afku a hanyar Kaduna zuwa Zariya.

Kwamandan hukumar kiyaye hadurra ta kasa reshen jihar Kaduna, Kabir Nadabo, ya ce hatsarin ya afku ne a tashar Aliko da ke kan hanyar Kaduna zuwa Zariya a ranar Talata da misalin karfe 06:25 na safe.

Nadabo ya alakanta yawaitar haɗurran da suka yi da yin tukin ganganci, lamarin da ya janyo dakatar da zirga-zirgar ababen hawa na wani dan lokaci.

Sai dai ya ce hanyar a halin yanzu babu walwala da zirga-zirga, inda ya ce tawagar masu aikin ceto na Zebra 35 Rigachikun sun kai dauki cikin gaggawa inda suka kai dauki.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]