
Aƙalla mutane biyar aka tabbatar da sun mutu a yayin da aka ceto wasu mutane 10 da ransu bayan da wani ginin me hawa uku da ake tunawa ya ruguzo da safiyar ranar Asabar a kasuwar unguwar Durumi 3 dake kusa da Kasuwar Gudu a Abuja
Lere Olayinka mai taimakawa, Nyesom Wike ministan birnin tarayya Abuja kan hulda da jama’a da soshiyal midiya ya tabbatar da faruwar lamarin a cikin wani sako da ya fitar ranar Asabar a Abuja.
A cewar sanarwar jami’an kai daukin gaggawa sun isa wurin tare da gudanar da aikin ceto dai-dai lokacin da ake fargaban cewa akwai mutane da dama a kasan baraguzan gini.
“Aƙalla mutane biyar aka tabbatar sun mutu a yayin da aka ceto wasu mutanen 10 da ransu bayan da ginin bene mai hawa uku da ake ginawa ya ruguzo a yankin Durumi 3 kusa da Kasuwar Gudu dake Abuja ranar Asabar da safe,” a cewar sanarwar.
Sanarwar ta kara da cewa Mr Wike ya bayar da umarnin kula da lafiya kyauta ga mutanen da abin ya shafa.

