An yi garkuwa da wasu yan ƙasar China biyu a Kwara

Yan bindiga sun yi garkuwa da wasu Sinawa biyu daga wani wuri da su ke aikin ginin hanya a jihar Kwara.

Mutanen na daga cikin ma’aikata yan kasar waje dake aikin ginin hanyar Bode Saadu-Kaiama-Kosubosu da kamfanin BUA ke gudanarwa lokacin da yan bindigar da fuskarsu ke a rufe suka isa wurin inda suka rika harbin kan me uwa da wabi.

Lamarin ya faru ne a ranar Litinin a wurin aikin dake Ejidongari a karamar hukumar Moro ta jihar.

Adekimi Ojo kwamishinan yan sandan jihar shi ne ya tabbatarwa jaridar The Cable faruwar haka a ranar Juma’a.

” Eh gaskiya ne an yi garkuwa da wurin aikin ginin titi  suna aiki ne da kamfanin BUA abin da zan iya fada kenan a yanzu,” ya ce.

A yan makonnin  nan dai ana cigaba da samun yawan ƙaruwar garkuwa da mutane da kuma hare-haren yan bindiga a jihar ta Kwara

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]