An yi garkuwa da wasu yan ƙasar China biyu a Kwara

Yan bindiga sun yi garkuwa da wasu Sinawa biyu daga wani wuri da su ke aikin ginin hanya a jihar Kwara.

Mutanen na daga cikin ma’aikata yan kasar waje dake aikin ginin hanyar Bode Saadu-Kaiama-Kosubosu da kamfanin BUA ke gudanarwa lokacin da yan bindigar da fuskarsu ke a rufe suka isa wurin inda suka rika harbin kan me uwa da wabi.

Lamarin ya faru ne a ranar Litinin a wurin aikin dake Ejidongari a karamar hukumar Moro ta jihar.

Adekimi Ojo kwamishinan yan sandan jihar shi ne ya tabbatarwa jaridar The Cable faruwar haka a ranar Juma’a.

” Eh gaskiya ne an yi garkuwa da wurin aikin ginin titi  suna aiki ne da kamfanin BUA abin da zan iya fada kenan a yanzu,” ya ce.

A yan makonnin  nan dai ana cigaba da samun yawan ƙaruwar garkuwa da mutane da kuma hare-haren yan bindiga a jihar ta Kwara

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]