ZaÉ“aÉ“É“un Æ´an majalisar wakilai ta tarayya da aka zaba karkashin jam’iyyun adawa wandanda suka yi wa kansu laÆ™abin ‘Greater Majority’ a turance yanzu haka kansu ya rarrabu kan yan takarar shugaba da kuma mataimakin shugaban majalisar dattawa.
Ƙungiyar Greater Majority na da mambobi da suka fito daga jam’iyyun adawa 7 a majalisar wakilai ta 10 da ake shirin kafawa.
Jam’iyun sun haÉ—a da PDP, Labour Party(LP) APGA, NNPP, YPP,SDP da kuma ADC.
Ƙungiyar sun gudanar da taruka biyu a lokaci guda a otal ɗin Transcorp Hilton da kuma Frazier Suites dake Abuja a daren ranar Litinin domin lalubo mafita akan lamarin.
Amma kuma tarukan sun fito da mabanbantar matsaya a yayin da É“angare É—aya ya goyi bayan É—antakar sulhu na jam’iyyar APC, Hon Tajuddeen Abbas(APC Kaduna)da Benjamin Kalu(APC Abia) a matsayin shugaba da mataimaki.
A karshen kammala taron na otal É—in Transcorp Hilton wata sanarwa mai É—auke da sahannun sakataren taron, Kabiru Alahsan Ruwa da kuma shugaban taron Idu Igariwey ta bayyana cewa sun yanke shawarar haÉ—e kan su domin goyon bayan Abbas.
Amma kuma a taron da aka gudanar a otal É—in Frazier Suites, Victor Afam Ogene wanda ya bayyana matsayar taron ya ce ba su da wani takamaiman É—an takara da suke goyon baya tun da babu wanda ya tsaya takarar daga jam’iyyun adawa.