An sake kama wasu daga cikin fursunonin da suka tsere a Benin – AREWA News

Rundunar yan sandan jihar Edo ta sake kama wasu daga cikin daurarrun da suka tsere daga gidajen yarin da aka balle a yayin zanga-zangar EndSARS a jihar.

Shida daga cikin wadanda suka tsere an kama su ne da laifin aikata fashi da makami a yayin da aka kama mutum daya lokacin da yake kokarin kisan mutumin da ya bada sheda akan sa a gaban kotu.

Daurarrun su goma na daga cikin mutane 120 da rundunar ta kama da ake zargi da hannu a fasawa tare da daka wawa na kayan abinci da ma wasu kayayyaki a ofishin hukumar kwastam da kuma wasu rumbunan ajiye kayayyakin abinci na wasu kamfanoni dake jihar.

Kwamishinan yan sandan jihar,Johson Kokuman ya bayyana sunan daurarrun da aka sake kamawa da suka hada da Emmanuel Udoh, Friday Etim, Victor Akpotor, Lucky Precious, Osarumen Enoragbon, Patrick Eguavoen, Abraham Matthew, Endurance Ifobuow, Mohammed Adamu da Henry Atadi.

Ya ce Henry Atadi bayan tserewarsa daga gidan yarin ya samu nasarar kwace wata mota kirar Lexus inda aka kama shi da ita a Okada.

More News

Matatar mai ta fatakwal za ta iya fara aiki a ƙarshen watan Yuni

Matatar mai ta Fatakwal mai tace mai ganga 210,000 a kowacce rana na iya fara aiki a karshen watan Yuli bayan dogon lokaci. Jami’in hulda...

Peter Obi Ya Ziyarci Mutanen Da Su Ka Ƙone Sakamakon Wutar Da Wani Ya Cinnawa   Masallaci A Kano

Ɗan takarar shugaban ƙasa  a zaɓen 2023 ƙarƙashin jam'iyar Labour Party (LP) Peter Obi ya ziyarci mutanen da wani matashi ya cinnawa wuta a...

An sanar da zaman makoki na kwana biyar saboda mutuwar shugaban kasa a Iran

Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya sanar da zaman makoki na kwanaki biyar saboda rasuwar shugaban kasar Ibrahim Raisi...

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...