An kama ƴan kungiyar IPOB 18 da ake zargi da kisan ƴan sanda

Rundunar yan sandan jihar Imo ta kama mutane 18 da ake zargi da zama yan kungiyar IPOB da suke da hannu a kisan ƴan sanda biyu a mahadar Ahiara dake karamar hukumar Ahiazu-Mbaise ta jihar.

Jami’an tsaron da suka tsaya shan mai a gidan man BOEK Petroleum a ranar Litinin sun fuskanci farmaki daga wasu ƴan bindiga da ake zargin ƴan IPOB ne.

Maharan na sanye ne da kayan sojoji inda suka farma ƴan sandan babu zato dake motoci uku kuma suka riƙa harbin kan me uwa da wabi.

A cewar Henry Okoye mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar ya ce yan sandan biyu da aka kashe a harin sun haɗa da DPO na Ahiazu-Mbaise da kuma wani insifecta.

Ya ce mutanen na cigaba da amsa tambayoyi a yayin da ake cigaba da bincike.

More News

Sojan Jamhuriyar Nijar sun kama Gawurtaccen Ɗan Fashin dajin Najeriya Kachalla Mai Daji

Dakarun sojan Jamhuriyar Nijar sun samu nasara kama gawurtaccen ɗan fashin dajin nan mai suna Kachalla Mai Daji a garin Illela dake kan iyakar...

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraɗiyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...