Rundunar Ruwa Ta Najeriya Ta Mika Wasu Da Ake Zargi Ƴan IPOB Ne Ga DSS a Anambra



Rundunar Ruwa ta Najeriya ta miƙa wasu mutum biyar da ake zargin suna da alaƙa da ƙungiyar IPOB da ESN ga Hukumar Tsaro ta DSS reshen jihar Anambra domin ci gaba da bincike.

A wata sanarwa da Daraktan Yaɗa Labarai na rundunar, Abiodun Folorunsho, ya fitar, an ce jami’an rundunar da ke Onitsha ne suka kama mutanen bayan samun bayanan sirri da suka danganta su da ayyukan laifi a ƙaramar hukumar Ogbaru.

Binciken farko ya nuna cewa ɗaya daga cikin waɗanda aka kama na jagorantar ayyukan ƙungiyar a wasu yankuna, yayin da sauran ake zargin suna da alaƙa da cibiyar.

Rundunar ta ce binciken ya kuma gano wuraren da ake zargin ana amfani da su wajen tarurruka da ɗaukar sababbin mambobi.

Ta bayyana cewa an miƙa mutanen ga DSS ne domin ci gaba da bincike da ɗaukar matakan da suka dace.

More from this stream

Recomended