An Jikkata Jami’an Tsaro A Harin Da Ƴan Bindiga Su ka Kai Wa Ayarin Motocin Yahaya Bello

A jikkata wasu jami’an tsaro a wani hari da yan bindiga su ka kai kan jerin ayarin motocin gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ranar Asabar akan hanyar Abuja zuwa Lokoja.

Kingsley Fanwo, kwamishinan yaɗa labarai na jihar ya ce an kai harin ne a kusa da sansanin sojojin ruwa dake da tazarar ƴan kilomitoci daga Lokoja babban birnin jihar.

Kwamishinan ya ce lamarin da ya faru da misalin karfe 12:30 na rana ya jikkata mutane da dama ciki har da jami’an tsaro.

“Mun godewa Allah gwamnan mu ya bar wurin ba tare da ko kwarzane ba kuma babu dalilin shiga cikin firgici.” A cewar Fanwo.

More News

Rundunar Sojan Najeriya Ta Fitar Da Sunayen Sojojin Da Aka Kashe A Jihar Delta

Rundunar sojan Najeriya ta fitar da hoto da kuma sunayen sojoji 16 da aka yiwa kisan gilla a jihar Delta. Ranar Alhamis ne aka kashe...

Wasu ƴan mata a Najeriya sun ƙirƙiro janareta mai amfani da fitsarin mutum

Wasu matasa ‘yan Najeriya hudu sun kirkiro wani janareta mai amfani da litar fitsari don samar da wutar lantarki ta sa’o’i shida. Ƴan matan –...

Wasu ƴan mata a Najeriya sun ƙirƙiro janareta mai amfani da fitsarin mutum

Wasu matasa ‘yan Najeriya hudu sun kirkiro wani janareta mai amfani da litar fitsari don samar da wutar lantarki ta sa’o’i shida. Ƴan matan –...

Wasu ƴan mata a Najeriya sun ƙirƙiro janareta mai amfani da fitsarin mutum

Wasu matasa ‘yan Najeriya hudu sun kirkiro wani janareta mai amfani da litar fitsari don samar da wutar lantarki ta sa’o’i shida. Ƴan matan –...