An Jikkata Jami’an Tsaro A Harin Da Ƴan Bindiga Su ka Kai Wa Ayarin Motocin Yahaya Bello

A jikkata wasu jami’an tsaro a wani hari da yan bindiga su ka kai kan jerin ayarin motocin gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ranar Asabar akan hanyar Abuja zuwa Lokoja.

Kingsley Fanwo, kwamishinan yaɗa labarai na jihar ya ce an kai harin ne a kusa da sansanin sojojin ruwa dake da tazarar ƴan kilomitoci daga Lokoja babban birnin jihar.

Kwamishinan ya ce lamarin da ya faru da misalin karfe 12:30 na rana ya jikkata mutane da dama ciki har da jami’an tsaro.

“Mun godewa Allah gwamnan mu ya bar wurin ba tare da ko kwarzane ba kuma babu dalilin shiga cikin firgici.” A cewar Fanwo.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]