An gano gawar wani ɗan jarida da ya ɓace a Zamfara

An gano gawar Hamisu Danjibga wani ɗan jarida a jihar Zamfara da aka bada rahoton bacewarsa kwanaki uku da suka wuce a cikin ramin masai.

Danjibga na aiki ne da g kafar yada labarai ta Muryar Najeriya.

Ibrahim Ahmad sakataren kungiyar yan jarida ta NUJ reshen jihar Zamfara shi ne ya sanar da haka a ranar Laraba.

Ahmad ya ce yan makarantar islamiya ne dake wucewa suka bayyana cewa suna jin wani irin wari ta wurin abun da ya kai da hake ramin masai dake bayan gidan marigayin.

Sakataren kungiyar ya yi kira ga jami’an tsaro sun gudanar da bincike dan ganin sun gano waɗanda suka aikata haka.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]