An gano gawar Hamisu Danjibga wani ɗan jarida a jihar Zamfara da aka bada rahoton bacewarsa kwanaki uku da suka wuce a cikin ramin masai.
Danjibga na aiki ne da g kafar yada labarai ta Muryar Najeriya.
Ibrahim Ahmad sakataren kungiyar yan jarida ta NUJ reshen jihar Zamfara shi ne ya sanar da haka a ranar Laraba.
Ahmad ya ce yan makarantar islamiya ne dake wucewa suka bayyana cewa suna jin wani irin wari ta wurin abun da ya kai da hake ramin masai dake bayan gidan marigayin.
Sakataren kungiyar ya yi kira ga jami’an tsaro sun gudanar da bincike dan ganin sun gano waɗanda suka aikata haka.