An ƙona gidaje da dama a garin da aka kashe sojoji 16 A jihar Delta

Gidaje da dama ne dake garin Okuoma a gaÉ“ar ruwa aka Æ™one Æ™asa da sa’o’i 24 da kisan sojoji 16 a garin bayan da suka je kwantar da wani rikicin kabilanci.

Tukur Gusau daraktan yaÉ—a labarai a ma’aikatar tsaron Æ™asa a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar ya ce sojojin da suka haÉ—a Laftanal Kanal, Manjo 2   Kaftin guda É—aya da kuma  wasu sojoji 12 wasu matasa ne suka kashe su a ranar Alhamis.

Sojojin sun je garin ne biyo bayan kiran kai É—aukin gaggawa da aka yi masu sakamakon rikicin kabilanci tsakanin garuruwan Okuoma da Okoloba a jihar Delta.

Tuni babban hafsan hafsosin sojan  Najeriya, Christopher Musa ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan kisan.

A wani hoton bidiyo da gidan Talabijin na Channels ya wallafa ya nuna wasu gidaje dake garin suna ci da wuta.

Tuni mazauna garin da dama suka tsere saboda fargabar ramuwar gayya daga sojojin.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...