Gidaje da dama ne dake garin Okuoma a gaÉ“ar ruwa aka Æ™one Æ™asa da sa’o’i 24 da kisan sojoji 16 a garin bayan da suka je kwantar da wani rikicin kabilanci.
Tukur Gusau daraktan yaÉ—a labarai a ma’aikatar tsaron Æ™asa a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar ya ce sojojin da suka haÉ—a Laftanal Kanal, Manjo 2 Kaftin guda É—aya da kuma wasu sojoji 12 wasu matasa ne suka kashe su a ranar Alhamis.
Sojojin sun je garin ne biyo bayan kiran kai É—aukin gaggawa da aka yi masu sakamakon rikicin kabilanci tsakanin garuruwan Okuoma da Okoloba a jihar Delta.
Tuni babban hafsan hafsosin sojan Najeriya, Christopher Musa ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan kisan.
A wani hoton bidiyo da gidan Talabijin na Channels ya wallafa ya nuna wasu gidaje dake garin suna ci da wuta.
Tuni mazauna garin da dama suka tsere saboda fargabar ramuwar gayya daga sojojin.