An samu tashin hankali tsakanin Amurka da Iran bayan ƙasashen biyu sun kai wa juna hare-hare a Gabas ta Tsakiya, lamarin da ya barazana ga yarjejeniyar tsagaita wuta ta wucin gadi da ake ƙoƙarin tabbatarwa.
Sojojin Amurka sun ce sun ɗauki matakin kare kai bayan an kai wa jami’ansu hari da jirage marasa matuƙa, inda suka harbo guda huɗu.
A martaninta, Iran ta ce dakarun juyin juya halinta sun kai hari kan wani sansanin sojin Amurka a yankin, duk da cewa ba ta bayyana inda sansanin yake ba.
Rahotanni sun kuma ce an ji ƙarar gargaɗin hare-haren sama a ƙasar Kuwait.
Kafafen yaɗa labaran Iran sun ce wasu jiragen ruwa sun yi ƙoƙarin bi ta Mashigar Hormuz ba tare da neman izini daga Tehran ba, lamarin da ya sa sojojin Iran suka harba makaman gargaɗi.
Amurka Da Iran Sun Kai Wa Juna Hare-Hare A Gabas Ta Tsakiya

