Ministan Ayyuka, Dave Umahi, ya ce yana da yakinin cewa Allah zai ci gaba da bai wa Shugaba Bola Tinubu jagoranci har zuwa shekarar dubu biyu da talatin da ɗaya.
Umahi ya bayyana haka ne ranar Alhamis yayin duba ayyukan gadoji da ake gudanarwa a jihar Legas, ciki har da gadar Carter Bridge da ake shirin sake gina ta daga mako mai zuwa.
Ministan ya ce gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da samun taimakon Allah wajen magance matsalolin Najeriya, musamman matsalar rashin tsaro.
Ya kuma bukaci ’yan Najeriya su hada kai da gwamnatin tarayya domin dawo da zaman lafiya da tsaro a fadin kasar nan.
Umahi ya ce duk wani shugaba yana son zaman lafiya a mulkinsa, amma dole ne ya fuskanci kalubale idan sun taso.
Haka kuma ya nuna kwarin gwiwar cewa ayyukan da gwamnatin Tinubu ta fara za su kammala cikin nasara, yayin da aikin sake gina Carter Bridge ake sa ran zai dauki kimanin shekara uku.
Allah Zai Ci Gaba Da Tallafa Wa Tinubu Har Zuwa 2031 – Umahi

