Abin da ya sa Æ´an Najeriya da ke tsare a Saudiyya suka yi yajin cin abinci

Twiiter/Garba Shehu

Wasu ‘yan Najeriya da ke tsare a gidajen yarin Saudiyya sun koka kan mawuyacin halin da suke ciki tsawon watanni tun bayan kama su, da nufin izo Æ™eyarsu zuwa gida.

Sun dai yi iƙirarin cewa sun kai ɗaruruwa a gidajen yarin da ke Jeddah da Riyadh, cikinsu har da mata da ƙananan yara.

Mutanen da ke tsaren sun faɗa wa BBC cewa har yajin cin abinci sun yi don sanar da mahukunta halin da suke ciki, amma a duk lokacin da suka tuntuɓa sai a faɗa musu cewa aikin kwaso su yana hannun ofishin jakadancin Najeriya.

A cewar É—aya daga cikinsu “aÆ™alla mun kai kimanin wata huÉ—u zuwa wata shida kuma aÆ™alla mata za su kai É—ari uku da wani abu, tsakaninmu da su akwai tazara kuma maganar yajin aikin cin abinci tabbas mun yi”.

Shi ma wani da ya kasance cikin wannan hali ya bayyana cewa sun shiga wani hali mawuyaci har ma a cikinsu a kwai tsofaffi in da ya ce “wani ma tsohon da Æ™yar yake tashi”.

Sun dai ce abin da kawai suke nema a yanzu shi ne gwamnati ta kai musu ɗauki domin fitar da su daga ƙangin da suke ciki ta hanyar mayar da su gida.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...