Abdulkarim Chukkol daraktan gudanarwa a hukumar EFCC mai yaÆ™i da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta’annati ya kama aiki a matsayin shugaban riko na hukumar.
A ranar Laraba ne shugaban kasa,Bola Ahmad Tinubu ya dakatar da shugaban hukumar, Abdulrashid Bawa ya kuma bada umarnin a bincike shi kan yadda ya jagoranci hukumar.
Daga bisani hukumar DSS ta gayyaci Bawa inda ya amsa tambayoyi kan wasu batutuwa.
A wata sanarwa ranar Alhamis hukumar ta ce Chukkol na daga cikin ma’aikatan da aka kafa hukumar da su.