
Mataimakin dan takarar shugaban kasa na Nigeria Democratic Congress (NDC), Rabi’u Kwankwaso, ya bukaci dan takarar shugaban kasa na African Democratic Congress (ADC), Atiku Abubakar, da ya janye burinsa na neman shugabancin Najeriya a 2027 tare da marawa NDC baya.
Kwankwaso ya yi wannan kiran ne ranar Alhamis lokacin da ya karbi bakuncin mambobin Kungiyar Fulani Farmers Association a gidansa da ke Abuja.
Tsohon gwamnan Kano ya bukaci Atiku ya janye daga takarar domin bai wa NDC damar tsayawa takarar shugaban kasa, inda ya tabbatar masa cewa za a kula da shi idan jam’iyyar ta samu nasarar lashe zaben.
“Step down for us; if we win, we will take care of you,” in ji Kwankwaso.
Kiran na Kwankwaso na zuwa ne yayin da ‘yan siyasar adawa ke kokarin hada karfi wuri guda domin kalubalantar Shugaba Bola Tinubu da jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a zaben 2027.
Atiku, wanda tsohon mataimakin shugaban kasa ne, na daga cikin fitattun ‘yan siyasar adawa da ke neman takarar shugaban kasa a 2027.
Kwankwaso da dan takarar shugaban kasa na NDC, Peter Obi, sun kasance cikin ‘yan siyasar da a baya suke da alaka da ADC kafin su fice daga jam’iyyar a watan Mayu.
Sun danganta ficewarsu da rikice-rikicen cikin gida da kuma shari’o’in kotu da suka dabaibaye jam’iyyar.
Ficewarsu zuwa NDC ya kara sauya alakar ‘yan siyasar adawa yayin da zaben shugaban kasa na 2027 ke kara karatowa.