Jam’iyar APC za ta cigaba da mulki har bayan shekarar 2031

Karamar ministar Babban Birnin Tarayya Abuja, Mariya Mahmud, ta bayyana cewa jam’iyyar All Progressives Congress (APC) za ta ci gaba da mulkin Najeriya har bayan shekarar 2031.

Ministar ta bayyana haka ne a yayin kaddamar da kungiyar City Boy Movement (CBM) a Kano a ranar Litinin, Mahmud ta shaida wa mahalarta taron cewa babu gurbin zama a Villa har zuwa 2031. 

Ta bayyana kungiyar amatsayin wani bigire da zai  hada matasa da mata a tun daga tushe domin tabbatar da sake zaben Tinubu da kuma ci gaba da  ɗorewar rinjayen da  APC take da shi. 

“Yawan matasa a Najeriya ya kai kusan kashi 60 zuwa 70 cikin dari. Idan kana son cimma wani abu kuma ka bar matasa masu iya aiki a baya, ba za ka yi nasara ba. Shi ya sa wannan bigire  ya samu kafuwa domin hada kowa, ya kuma  bayyana wa jama’a manufofin Mai Girma Shugaban Kasa,” in ji ta. 

Bunkure ta kawo misalai da gyare-gyare a Abuja da kuma shirin rancen dalibai (NELFUND) a matsayin nasarorin da za su yi wa Tinubu magana a lokacin zabe. 

Mahmud ta kuma yaba wa CBM saboda shigar da mata cikin tafiyar, tana mai cewa rawar da mata za su taka na da matukar muhimmanci ga nasarar jam’iyyar. 

A yayin taron, shugabannin CBM sun bayyana shirin fadada kungiyar zuwa mambobi miliyan 10 a fadin kasar. 

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...