

Nasiru Marafa, akawun jami’ar karatu ta daga ta National Open University of Nigeria (NOUN), ya rasu.
Oladipo Ajayi, matakaradar jami’ar ta NOUN kuma sakatare kwamitin gudanarwar jami’ar ne ya sanar da mutuwar Marafa a cikin wata sanarwa a ranar Lahadi, inda ya ce ana zargin ƴan bindiga ne suka harbe shi a lokacin da yake komawa daga Gusau, babban birnin jihar Zamfara.
“Shugaban Jami’ar , a madadin Kwamitin Gudanarwa, Hukumar Gudanarwa, Majalisar Malamai, Ma’aikata da Daliban Jami’ar National Open University of Nigeria (NOUN), na alhinin sanar da mutuwar akawun jami’ar, Mallam Nasiru Gusau Marafa, wanda ya rasu a yau, Lahadi, 6 ga Satumba, 2026,” a cewar sanarwar.
“Bisa ga bayanan da Jami’ar ta samu, an yi zargin an harbe Mallam Nasiru Gusau Marafa a lokacin da yake komawa daga Gusau.”
An nada Marafa a matsayin akawun jami’ar a ranar 17 ga Satumba, 2022, inda zai yi wa’adi na shekaru biyar da zai ƙare a Satumba 2027.
Ajayi ya bayyana marigayi a matsayin ma’aikaci mai sadaukarwa da himma na jami’ar, wanda ya yi aiki da kyau a cikin jami’ar kuma ya rike mukamai daban-daban a lokacin aikinsa.