
Rundunar sojojin Najeriya ta kama wani matashi mai shekaru 20, Bacha Modu Isah, da ake zargi da yi wa ƴan ta’adda leƙen asiri tare da haɗa kai da su a Ngamdu, ƙaramar hukumar Kaga ta Jihar Borno.
Sojojin Bataliya ta 154 Task Force Battalion ne suka gudanar da aikin tare da haɗin gwiwar jami’an Forest Guards da ƴan sa-kai na Civilian Joint Task Force (CJTF).
Majiyoyin tsaro sun ce an kama Isah da misalin ƙarfe 10:10 na dare ranar 2 ga Satumba 2026, bayan jami’an tsaro sun samu sahihan bayanan sirri.
An ce sojojin sun kwato wasu abubuwa daga hannunsa, ciki har da laya, abin kunna wuta, zobe da wani kayan fata.
A halin yanzu, ana tsare da wanda ake zargin a hannun sojoji domin ci gaba da gudanar da bincike.
Kamen na daga cikin matakan da hukumomin tsaro ke ɗauka domin gano tare da tarwatsa masu leƙen asiri, masu taimaka wa ƴan ta’adda da kuma hanyoyin tallafa musu a cikin al’ummomin yankin.