Sojoji Sun Ceto Mutane 25 Da Aka Yi Gqrkuwq Da Su A Katsina Da Zamfara



Rundunar Operation Fansan Yamma ta ce dakarunta sun ceto mutane 25 da ’yan ta’adda suka yi garkuwa da su a wasu ayyukan soji da aka gudanar a jihohin Katsina da Zamfara.

Jami’in yaɗa labaran rundunar, Laftanar Kanal Aliyu Danja, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a daren Juma’a.

Ya ce an ceto mutanen ne ranar Alhamis yayin da sojoji ke gudanar da sintiri da hare-haren yaƙi da ’yan ta’adda a jihohin biyu.

A Jihar Katsina, sojojin Sector 1 sun yi arangama da ’yan ta’adda yayin wani sintiri da daddare a Kwanar Kura, cikin ƙaramar hukumar Sabuwa.

Danja ya ce sojojin sun yi wa ’yan ta’addan ruwan wuta, lamarin da ya tilasta musu tserewa zuwa cikin daji.

Dakarun sun bi hanyoyin da ’yan ta’addan suka bi yayin tserewarsu, inda suka ceto mutane biyu da aka yi garkuwa da su a hanyar Dandume zuwa Damari.

Ya ce sojojin sun kuma kwato babura biyu mallakar ’yan ta’addan da suka tsere.

A Jihar Zamfara kuwa, sojojin Sector 2 sun ceto mutane 23 a lokacin wani samame a wajen garin Wuya, cikin ƙaramar hukumar Anka.

Danja ya ce waɗanda aka ceto sun ƙunshi maza uku da mata 20, kuma binciken farko ya nuna cewa ’yan ta’addan sun sace su ne a ƙaramar hukumar Gummi, inda suka shafe kusan makonni uku a hannunsu.

Ya ce an kwashe waɗanda aka ceto domin ba su kulawar lafiya tare da ci gaba da yi musu tambayoyi.

Rundunar ta ce nasarar aikin na nuna ci gaba da ƙoƙarin sojoji wajen kare fararen hula, dakile ayyukan ’yan ta’adda da kuma kuɓutar da mutanen da aka yi garkuwa da su.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...