

Dubban masu alhini, sarakunan gargajiya, shugabannin siyasa da kuma manyan baki da suka fito daga sassa daban-daban na Najeriya da kuma makotan ƙasashe sun tattaru a garin Gumel ranar Juma’a inda suka halarci jana’izar marigayi Sarkin Gumel, Alhaji Ahmad Muhammad Sani II wanda ya rasu yana da shekaru 85.
An gudanar da sallar jana’izar ne a fadar marigayin dake Masarautar Gumel da maraicen ranar Juma’a biyo bayan rasuwarsa a ƙasar Egypt ranar Alhamis 3 ga watan Satumba bayan da ya yi fama da jinya.
Marigayin wanda aka haifa a shekarar 1942 ya shafe gomman shekaru yana riƙe da masarautar dake da tsohon tarihi.
Jana’izar ta samu halartar mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima wanda ya wakilci tawagar gwamnatin tarayya da kuma gwamnan jihar Jigawa, Umar Namadi.
Marigayin ya rasu ya bar ƴaƴa 33 maza 21 da kuma mata 12 da kuma jikoki da dama.