Jami’in ɗan sanda ya faɗi ya rasu a yayin motsa jiki

Sulaiman SaadArewaHausa22 minutes ago

Wani Insifetan  ‘yan sanda da ke aiki da  rundunar ‘yan sanda ta Jihar Sokoto  ya rasu bayan ya yanke jiki ya faɗi ƙasa da sauri bayan kammala atisayen motsa jiki na mako-mako na rundunar.


Marigayin mai suna Adamu Isah, yana aiki ne  a sashen gudanarwa na rundunar.


A cewar sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar yan sandan jihar Sokoto, DSP Ahmad Rufa’i, ya fitar da ita a ranar Alhamis, ta ce  Isah ya yanke jiki ya faɗi ƙasa da sauri bayan ya dawo daga atisayen da aikawa lakabi da Walkathon a turance da ake gudanarwa a kowane mako ranar Laraba a hedkwatar rundunar.


An kai shi asibiti nan da nan, inda likitocin da ke kulawa da shi daga baya suka tabbatar da cewa ya rasu.


Kwamishinan ‘yan sanda, CP Hayatu Hassan Shaffa, ya nuna bakin ciki kan mutuwar fuju’a da  jami’in ya yi, yana mai bayyana shi a matsayin ɗan sanda mai sadaukarwa da ƙarfin hali wanda ya yi hidima ga ƙasa da himma da ƙwarewa.


Shaffa ya ce Isah kuma ɗan wasa ne mai himma kuma memba na ƙungiyar wasan volleyball ta rundunar, sannan kuma ɗan wasan dambe ne.


Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...