
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya yi Allah-wadai da hare-haren ‘yan bindiga da suka afku a wasu sassan jihar, tare da alkawarin daukar karin matakan tsaro domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
A wata sanarwa da Babban Daraktan Yada Labaran Gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar, an ce hare-haren sun shafi Chiromawa a Karamar Hukumar Garun Mallam, Beli a Rogo, Bebeji da wasu yankunan da ke kusa da Gwarzo.
Gwamnan ya jajanta wa wadanda abin ya shafa da iyalansu, yana mai bayyana hare-haren a matsayin abin takaici da ba za a amince da su ba.
Ya umurci hukumomin da abin ya shafa da su kara kaimi wajen tattara bayanan sirri, sa ido da kuma gaggauta kai dauki a wuraren da abin ya shafa.
Gwamnan ya ce, “Gwamnati za ta dauki matakan da suka dace domin kara tsaurara tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.”
Ya kuma bukaci jama’a su kwantar da hankula tare da bai wa jami’an tsaro cikakken hadin kai, musamman ta hanyar samar da sahihan bayanai da za su taimaka wajen gano tare da cafke wadanda ke da hannu a hare-haren.