Rikici Ya Lalata Makarantu 1,400, Ya Kashe Malamai 2,295 A Arewa Maso Gabas



Gwamnatin Jihar Borno ta bayyana cewa sama da makarantu 1,400 sun lalace a yankin Arewa maso Gabas sakamakon shekaru na rikice-rikicen tsaro, yayin da aka kashe malamai 2,295 tare da raba wasu 19,000 da muhallansu.

Mataimakin Gwamnan Borno, Umar Usman Kadafur, ne ya bayyana hakan a Maiduguri yayin taron kasa na kwanaki biyu kan tasirin rikice-rikice ga tunanin yara a Najeriya.

Kadafur ya ce kusan yara miliyan uku na bukatar tallafin ilimi na gaggawa, yayin da illar rikicin ke ci gaba da shafar tunaninsu, dabi’unsu da makomarsu.

Ya ce, “Raunin tunani ba ya kare idan bindigogi suka yi shiru. Yana shiga cikin kwakwalwarsu da ke ci gaba da bunkasa. Yana sauya fahimtarsu, dabi’unsu da kuma damar da suke da ita ta amincewa da mutane.”

Mataimakin gwamnan ya yi gargadin cewa rashin kula da matsalolin tunanin yaran da rikici ya shafa na iya jefa su cikin kiyayya, warewa daga al’umma da kuma yiwuwar kungiyoyin masu tayar da hankali su dauke su.

Ya bukaci gwamnati ta samar da tsarin kasa na kula da lafiyar kwakwalwar yaran da rikici ya shafa, tare da kara tura kwararru zuwa yankunan da matsalar ta fi kamari.

Daraktan Medical Intelligence, Dr Patience Omokri, wadda ta wakilci Mai Bai wa Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro, Nuhu Ribadu, ta ce ya kamata a dauki raunin tunanin yara a matsayin batun tsaron kasa.

A cikin sakon Ribadu, ya ce, “Yaron da ya samu rauni a tunaninsa ba wanda aka zalunta kawai ba ne. Idan ba a tallafa masa ba, zai iya zama tushen rashin zaman lafiya.”

UNICEF ta ce yara 270,864 a jihohin Borno, Adamawa da Yobe na bukatar tallafin lafiyar kwakwalwa da na zamantakewa karkashin shirin bukatun jin kai na shekarar 2026.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...