

An ba da rahoton cewa wasu mutane biyu da ake zargin ’yan kungiyar ISWAP ne sun mika wuya ga sojojin Najeriya a karamar hukumar Monguno ta jihar Borno.
A cewar Zagazola Makama, mujallar dake wallafa labarai kan yaki da ta’addanci a yankin tafkin Chadi da Najeriya baki ɗaya, ’yan uwa biyun da ake zargi, Jidda Modu, mai shekara 20, da Kaka Kawu, mai shekaru shekara 21, sun mika wuya ga dakarun sojan Hedikwatar Shiya ta 3 dake garin Monguno a ranar Talata.
Kafar ta jiyo majiyoyi na cewa ’yan uwa biyu sun mika bindigogin AK-47 guda biyu, harsashi guda takwas, da magazin guda biyu.
“Sauran kayan da aka kwato daga gare su sun hada da wayoyi guda biyar — Infinix, Tecno, Samsung, Redmi da Tecno mai madannai— tare da earbuds guda daya, power bank, katin ATM na bankin Zenith, katin memori da USB cable,” in ji mujallar.
Binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa mutanen biyu sun kasance cikin rukuni na kusan ’yan ISWAP 10 da suka bar sansanin ’yan ta’adda a Arinna Chiki da niyyar mika wuya ga hukumomi.”
Makama ya ce an kai ’yan uwa biyu da duk kayan da aka kwato zuwa Hedikwatar Sashen 3 don ci gaba da matakai.