Sojoji Sun Ceto Matar Tsohon Janar Kasa Da Sa’o’i 24 Bayan Sace Ta



Rundunar Sojojin Najeriya ta ceto Mrs Adonkie, matar Birgediya Janar Basil Adonkie, kasa da sa’o’i 24 bayan da masu garkuwa da mutane suka sace ta daga gidanta a Abuja.

An ce an sace matar ne a ranar Talata, 1 ga Satumba, 2026, lamarin da ya sa sojojin Guards Brigade da Army Headquarters Garrison suka fara wani samame na musamman domin gano inda take da kuma kubutar da ita.

A cewar sanarwar da rundunar ta wallafa a shafinta na Facebook, sojoji sun samu sahihan bayanan sirri sannan suka bi sawun masu garkuwar ta hanyar Aco Estate zuwa Goza Community.

Rundunar ta ce matsin lambar da sojojin suka yi wa masu garkuwar ya tilasta musu guduwa zuwa cikin dazuzzuka, inda suka bar wanda suka sace.

Daga bisani, an ceto Mrs Adonkie a Angwan Sabo Village, yayin da sojojin suka ci gaba da bin sawun wadanda suka sace ta tare da katange hanyoyin da za su iya amfani da su wajen tserewa.

A wani samame da aka gudanar ranar Laraba, 2 ga Satumba, sojoji sun cafke wasu mutane biyu da ake zargi da kasancewa cikin kungiyar masu garkuwa da mutane kusa da Gaube Village a Karamar Hukumar Kuje ta Abuja.

An kwato bindigar AK-47 guda daya, magazine guda daya da kuma harsasai 19 kirar 7.62mm Special daga hannun wadanda ake zargin.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...