
Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) reshen jihar Neja ta yi kira da a ƙara tsaurara matakan tsaro a wuraren ibada, musamman lokacin sallar Juma’a da bautar ranar Lahadi.
Kiran ya biyo bayan sace wasu Musulmai da mazauna ƙauyuka a gundumar Dekara, ƙaramar hukumar Borgu, inda ake zargin ’yan ta’adda sun kai hari tare da yin garkuwa da wasu masu ibada daga masallatai yayin sallar Juma’a.
Shugaban CAN na jihar Neja, Bishop Bulus Yohanna, ya bayyana hare-haren wuraren ibada a matsayin barazana ga dukkan al’umma, ba tare da la’akari da addinin waɗanda abin ya shafa ba.
Ya ce: “Hare-haren da ake kai wa wuraren ibada barazana ce ga al’umma baki ɗaya, ba tare da la’akari da addinin waɗanda abin ya shafa ba.”
Bishop Yohanna ya kuma jajanta wa al’ummomin Musulmin da lamarin ya shafa, yayin da gwamnatin tarayya da ta jihar Neja suka ce suna aiki tare da jami’an tsaro domin ceto waɗanda aka sace da kuma dawo da zaman lafiya a yankin.