

Jam’iyar All Progressive Grand Alliance( APGA) ta lashe kujeru 21 na dukkanin ƙananan hukumomin jihar Anambra da aka gudanar a ranar Asabar
Har ila yau jam’iyar ta lashe zaɓen dukkanin kujerun kansiloli dake faɗin jihar kamar yadda hukumar zaɓen jihar ta bayyana a ranar Lahadi.
Genevieve Osakwe shugabar hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Anambra, ANSIEC ce ta bayyana haka a ofishin hukumar dake Awka babban birnin jihar.
Osakwe ta ce jam’iyar APGA ta lashe zaɓen kujerun ƙananan hukumomin baki ɗaya tare da zaɓen kujerun kansiloli.
Ta ce hukumar zaɓen ta tattara sakamakon zaɓen cikin nutsuwa domin tabbatar da cewa ba a samu kuskure ba.
Ta kara da cewa zaɓen ya gudana lami lafiya a mazabu guda 362 dake fadin jihar.