Mutum 37 Sun Mutu Bayan Harin Rasha Kan Ma’ajiyar Makamai A Ukraine



Akalla mutum 37 sun mutu, yayin da kusan 400 suka bar gidajensu bayan wani harin jirage marasa matuƙa na Rasha ya afkawa wata ma’ajiyar makamai ta sojojin Ukraine a wajen birnin Kyiv.

Harin, wanda ya faru a daren Juma’a, ya haifar da fashe-fashe masu ƙarfi bayan harsasai, nakiyoyi da jiragen yaƙi marasa matuƙa da aka ajiye a ma’ajiyar suka tashi.

Fashewar ta lalata kusan gidaje 130 da ke kusa, ciki har da wata cibiyar kula da tsofaffi da masu nakasa. Mutum 42 kuma sun samu raunuka, ciki har da yara huɗu.

Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky, ya ce bai kamata a ajiye makamai masu fashewa a kusa da gidajen jama’a ba.

Zelensky ya ce: “Bai kamata a ajiye makamai masu fashewa a kusa da gidajen jama’a ba. Wannan babban sakaci ne.”

Ya kuma sanar da fara bincike kan jami’an da suka amince da adana makaman a yankin da ake zaune, yayin da masu aikin ceto ke ci gaba da gudanar da ayyukansu a yankin Bucha.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...