
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, zai bar Abuja domin yin hutun mako uku a Turai a matsayin wani ɓangare na hutun shekara-shekara.
A cewar sanarwar Fadar Shugaban Ƙasa, Tinubu zai fara da zuwa Landan, Birtaniya, kafin ya ci gaba da hutunsa.
Mai ba shugaban shawara na musamman kan yaɗa labarai da dabarun sadarwa, Bayo Onanuga, ya ce hutun zai kasance na aiki, inda shugaban zai ci gaba da gudanar da wasu ayyukan gwamnati daga wajen ƙasar.
Onanuga ya ce: “Hutun zai kasance hutun aiki, kuma shugaban zai ci gaba da gudanar da wasu ayyukan gwamnati yayin da yake wajen ƙasar.”
Sanarwar ta ce ana sa ran Tinubu zai dawo Najeriya bayan hutun domin mayar da hankali kan shirye-shiryen yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na Janairu 2027.