
Daraktan-Janar na Kwamitin Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa na jam’iyyar APC, Abdul’Aziz Yari, ya bayyana cewa Shugaba Bola Tinubu zai sake lashe zaben shugaban kasa na 2027.
Yari, wanda tsohon gwamnan Zamfara ne kuma Sanata mai wakiltar jihar, ya bayyana hakan ne a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja.
Ya ce APC na da yakinin cewa za ta ci gaba da rike mulkin kasar har bayan wa’adin Tinubu na biyu, idan ya samu nasarar sake zaben.
Maganar tasa ta biyo bayan kaddamar da kwamitin yakin neman zaben APC, wanda Tinubu zai jagoranta. Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, da Shugaban APC na kasa, Nentawe Yilwatda, na cikin manyan jami’an kwamitin, yayin da Gwamnan Imo, Hope Uzodimma, aka nada sakatare, Yari kuma darakta-janar.
Yari ya ce kwamitin zai yi aiki domin ganin an sake zaben Tinubu tare da tabbatar da cika alkawuran da APC ta dauka a lokacin yakin neman zaben 2023.
Ya kuma tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatin APC za ta cika alkawuran da ta yi wa jama’a.
Yari ya kuma yi addu’ar Allah ya bai wa Tinubu hikimar jagorantar kasar, tare da bayyana fatansa cewa APC za ta ci gaba da mulkin Najeriya bayan wa’adin Tinubu na biyu.