Sojoji Sun Kama Masu Safarar Makamai Guda Uku, Sun Kuma Ceto Mutane Shida A Zamfara

Muhammadu SabiuHausa19 minutes ago



Dakarun Rundunar Hadin Gwiwa ta Arewa maso Yamma, Operation FANSAN YAMMA, sun kama wasu mutane uku da ake zargi da safarar makamai tare da ceto mutane shida da aka yi garkuwa da su a wasu samame daban-daban a Jihar Zamfara.

A ranar Lahadi, 23 ga Agusta, 2026, sojojin sun kuma kwato bindigar AK-103-2, harsashi 30 da kuma jigidar harsashi guda daya.

Jami’in Yada Labarai na Rundunar, Laftanar Kanal Aliyu Danja, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin.

Ya ce dakarun Sector 2 sun tare wata mota dauke da mutane uku da ake zargi da safarar makamai a kan hanyar Kaura Namoda zuwa Shinkafi. Binciken motar ya gano bindigar da harsasan a boye cikin buhun gero.

Danja ya ce ana ci gaba da binciken wadanda ake zargin tare da makaman da aka kwato, yayin da suke hannun sojoji.

A wani samame na daban, sojojin sun mayar da martani ga kiran neman agaji bayan wasu ‘yan bindiga sun kai hari kan matafiya a hanyar Anka zuwa Gummi.

Ya ce sojojin sun yi artabu da maharan yayin da suke kokarin kai wadanda suka yi garkuwa da su cikin wani daji da ke kusa. Matsin lambar da sojojin suka yi ya tilasta wa maharan tserewa, inda suka bar dukkan wadanda aka yi garkuwa da su.


Rundunar ta ce samamen sun nuna kokarinta na dakile hanyoyin da kungiyoyin ‘yan ta’adda ke samun makamai tare da kare al’umma da masu amfani da hanyoyi a yankin Arewa maso Yamma.

Danja ya bukaci al’umma su ci gaba da kasancewa cikin taka-tsantsan tare da sanar da jami’an tsaro duk wani mutum, makami ko motsi da suke zargi.

Ya ce hadin kan jama’a na da muhimmiyar rawa wajen dakile ayyukan kungiyoyin ta’addanci da kuma tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi a yankin Arewa maso Yamma.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...