

Sanata Abdulaziz Yari ya bayyana cewa yana da yakinin shugaban ƙasa,Bola Ahmad Tinubu zai lashe zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.
Ya kuma bayyana cewa jam’iyar APC za ta cigaba da ɗarewa akan karagar mulkin Najeriya har ya zuwa bayan shekarar 2031.
Hakan na zuwa ne duk da ce-ce-kucen da ya biyo bayan ƙunshin sunayen mutanen da kwamitin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya kunsa.
Yari wanda shi ne zai jagoranci yaƙin neman zaɓen a matsayin darakta janar na kwamitin jam’iyar APC na yakin neman zaɓen shugaban ƙasa ya bayyana haka ne a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe dake Abuja jim kaɗan bayan saukarsa a filin daga wata tafiya da ya yi ƙasashen waje.
Ya samu tarba daga magoya bayan jam’iyyar APC waɗanda suka taru a filin jirgin domin yi masa barka da zuwa tare da addu’ar samun nasarar jam’iyar APC a zaɓen mai zuwa.