
’Yan bindiga sun kai hare-hare a wasu al’ummomi a jihar Zamfara, inda suka kashe mutane da dama, suka jikkata wasu tare da lalata gidaje da kadarori.
Hare-haren sun faru ne a yammacin Lahadi a Bardoki da ke ƙaramar hukumar Gummi da Bunkasau da ke ƙaramar hukumar Bukkuyum.
Wani mai sharhi kan harkokin tsaro, Bakatsine, ne ya bayyana lamarin a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X.
Ya ce ’yan bindigar sun kashe mutane tare da jikkata wasu, yayin da hare-haren suka tilasta wa mazauna yankunan tserewa domin tsira da rayukansu.
Ya kuma bayyana cewa wasu jami’an Civilian JTF da suka nufi Bunkasau domin mayar da martani kan harin sun fada cikin kwanton baunar ’yan bindigar.
Bayan harin Bardoki, ’yan bindigar sun kuma cinnawa al’ummar Ruwan-Kura wuta, lamarin da ya tilasta wa mazauna yankin barin gidajensu.
Rahoton ya ce wasu daga cikin mutanen da suka rasa matsugunansu sun tsere zuwa Daki Takwas, yayin da wasu suka nemi mafaka a Dargaje.