Masu Garkuwa Sun Nemi Naira Miliyan 17 Don Sakin Matashin Da Aka Sace Yayin Tafiya Zuwa NYSC

Muhammadu SabiuHausa10 minutes ago



Iyalin wani matashi mai shekara 28, Emmanuel Egbedi, daga Kaduna, sun roƙi hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki su taimaka wajen kubutar da shi daga hannun masu garkuwa da mutane.

An sace Emmanuel ne a ranar 5 ga Agusta yayin da yake tafiya zuwa sansanin NYSC bayan an tura shi domin fara aikin yi wa ƙasa hidima. Harin ya faru ne a kusa da Okpella a Jihar Edo.

Ɗan’uwansa, Adewale Egbedi, ya ce motar da Emmanuel yake ciki na ɗauke da fasinjoji 18, yayin da wasu daga cikinsu, ciki har da masu shirin fara NYSC, su ma aka sace. Ya ce an kuma kashe direban motar.

Adewale ya bayyana cewa masu garkuwar sun fara neman N100m a matsayin kuɗin fansa, amma bayan tattaunawa da iyalin sun rage kuɗin zuwa N20m, kafin daga bisani su ce za su karɓi N17m.

Ya ce iyalin ba su da wannan kuɗin, yayin da suke fargabar lafiyar Emmanuel saboda masu garkuwar kan kira su da dare tare da dukan waɗanda aka sace.

A cewarsa, iyalin sun kai rahoton lamarin ga hukumomin tsaro, ciki har da Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Edo, tare da ci gaba da neman hanyar da za a ceto Emmanuel da sauran waɗanda aka sace.

Adewale ya ce lamarin ya yi matuƙar shafar iyalin, musamman mahaifiyarsu wadda ta daina cin abinci saboda damuwa har sai da aka kwantar da ita a asibiti.

Ya ce babban abin da suke nema shi ne a dawo musu da Emmanuel da sauran waɗanda aka sace cikin ƙoshin lafiya.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...