Ƴanbindiga Sun Kai Hari A Kauyukan Neja, Inda Suka Afka Masallatai



Wasu ’yanbindiga sun kai hari a wasu kauyuka da ke karamar hukumar Borgu a jihar Neja, inda suka sace mutane da dama a lokacin da suke gudanar da Sallar Juma’a.

Mazauna yankin sun ce ’yanbindigar sun kai hare-haren a kauyukan Dekara, Gidan Zana, Sabon Gida da Masaka.

Danmajalisar tarayya mai wakiltar yankin, Hon. Jafar Muhammad Shetiman Borgu, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce har yanzu ba a iya tantance adadin mutanen da aka sace aka tafi da su cikin daji ba.

Danmajalisar ya kuma bayyana cewa wasu daga cikin masallatan da ke cikin wuraren ibadar an kashe su, lamarin da ya ce ya jefa al’ummar yankin cikin tsananin fargaba.

Ya ce al’ummar yankin na cikin tashin hankali sakamakon hare-haren.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...