Gwamnatin tarayya ta sanar da ranar hutun Maulidi

Sulaiman SaadHausa1 minute ago

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Talata 25 ga watan Agusta a matsayin ranar hutun  bikin Maulidin Annabi Muhammad (SAW)  na shekarar 2026.

Ministan ma’aikatar harkokin cikin gida, Olabunmi Tunji Ojo ne ya bayyana haka a madadin gwamnatin tarayya a cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Juma’a ta bakin babbar sakatariyar ma’aikatar, Magdalene Ajani.

Ministan ya taya al’ummar Musulmin Najeriya dama wanda suke kasashen waje murnar bikin inda ya ya shawarce  su suyi amfani da bikin wajen yin koyi da halaye da darussa dake tattare da rayuwar manzon Allah Annabi Muhammad SAW.

Tunji-Ojo ya ce bikin ya bawa yan Najeriya dama na su ɗauki wasu darussa daga rayuwar manzon Allah musamman tausayi, ƙanƙan da kai da kuma kyautatawa al’umma.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...