
Shugabannin ƙungiyoyin mata a karkashin shirin FG/IFAD Value Chain Development Programme (VCDP) sun yi kira ga gwamnatin jihar Neja da ta ƙara tallafa wa mata manoma domin su faɗaɗa ayyukan noma da inganta samar da abinci.
Shugabannin sun kuma buƙaci hukumomi su ƙara ƙoƙari wajen dakile safarar yara da auren wuri da ake yi wa ’yan mata a jihar.
Sun bayyana hakan ne a Bida yayin wani taron horas da shugabannin ƙungiyoyin mata, matasa da masu buƙata ta musamman kan dabarun shawarwari da neman sauye-sauye.
Matan sun ce tallafin gwamnati zai taimaka wajen bunƙasa noma da kuma ƙara wa mata damar tallafa wa iyalansu da al’ummominsu.
Sun kuma jaddada cewa safarar yara da auren wuri na buƙatar haɗin gwiwa tsakanin gwamnati, ƙungiyoyin al’umma da sauran masu ruwa da tsaki domin kare yara da ’yan mata.
Hajarat T. Mohammed da Priscilla Ibrahim, wadanda suka yi magana a madadin shugabannin mata, sun ce hulɗa kai tsaye da masu yanke hukunci na da muhimmanci wajen mayar da matsalolin da al’umma ke fuskanta zuwa matakan da za su kawo sauyi.
A nasa bangaren, Muhammad Abubakar Enagi, shugaban E.I. People with Disabilities Farmers Cooperative Society Ltd., ya yaba wa VCDP kan shigar da manoman da ke da nakasa cikin shirin.
Shi ma jami’in Gender Mainstreaming na VCDP a jihar, Hajiya Maimuna Abubakar Ahmed, ya ce horaswar na da nufin ƙarfafa ƙungiyoyin wajen yin hulɗa da masu yanke hukunci domin samun manufofi da albarkatun da za su magance matsalolinsu.