
Akalla mutum 48 ne suka rasa rayukansu a wani hatsarin kwale-kwale a yankin Goronyo na jihar Sokoto, yayin da ake ci gaba da neman yara 12 da suka ɓace bayan hatsarin.
Rahotanni sun ce mafi yawan waɗanda hatsarin ya rutsa da su yara ne da mata, waɗanda ke kan hanyar zuwa gonaki a safiyar Alhamis.
Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Gada da Goronyo, Bashir Gorau, ya ce masu aikin ceto na ci gaba da neman yaran da suka ɓace.
“Akasarin waɗanda abin ya rutsa da su yara ne da mata, yara ƴan ƙasa da shekara 10,” in ji Gorau.
Ya bayyana cewa mazauna yankin na amfani da kwale-kwale domin zuwa gonakinsu saboda rafi ya raba ƙauyuka da filayen noma.
Hatsarin kwale-kwale na yawan faruwa a Najeriya, musamman a lokacin damina, saboda cikar rafuka da ruwa, rashin kayan kariya da kuma amfani da kwale-kwalen da ba su da inganci.