Mutane Huɗu Ƴan Gida Ɗaya Sun Mutu Bayan Cin Abinci A Kogi



Mutane huɗu daga iyali guda sun mutu bayan cin abincin gargajiya mai suna amala a garin Ihima, ƙaramar hukumar Okehi ta Jihar Kogi.

Kwamishinan Yaɗa Labarai da Sadarwa na jihar, Kingsley Fanwo, ya bayyana cewa Gwamna Ahmed Ododo ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

Gwamnatin ta ce binciken zai mayar da hankali kan yiwuwar gubar abinci ko kuma gurɓacewar abincin da iyalin suka ci, tare da duba wasu abubuwan lafiya ko muhalli da ka iya haddasa mutuwar.

An kuma ce karen iyalin ya mutu bayan cin abincin, kuma gwamnati za ta sanya wannan lamari cikin abubuwan da za a bincika.

Fanwo ya buƙaci jama’a su kwantar da hankalinsu tare da guje wa yanke hukunci kan musabbabin mutuwar kafin hukumomi su kammala bincike.

Gwamnatin Kogi ta ce za ta sanar da jama’a sakamakon binciken da zarar ta samu sahihan bayanai.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...