Sojoji sun kama masu safarar bindiga a jihar Zamfara

Dakarun rundunar Sojan Najeriya na Birged ta 1 ƙarƙashin jagorancin Kwamandan rundunar Kanal J  Umaru dake aiki a rundunar Operation Fansan Yamma dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso yamma sun samu nasarar kama wasu masu safarar bindiga a jihar Zamfara.

A ranar 23 ga watan Agusta ne aka kama mutanen su uku a dai-dai lokacin da dakarun suke binciken ababen hawa akan titin Kauran Namoda- Shinkafi.

Mutanen da aka kama sun haɗa da Lukman Sulaiman  mai shekaru 20, Nafiu Isa mai shekaru 18 dukkansu  sun fito ne daga ƙauyen Yar Galadima dake gundumar Ɗan Sadau sai kuma Adamu Lawali mai shekaru 60 wanda shi ne direban motar hayar da su ke ciki.

A binciken da aka gudanar bayan tsayar da motar an gano bindiga kirar AK-103-2 tare da gidan zuba harsashi guda ɗaya da kuma harsashi guda 30 da aka ɓoye su a cikin buhun gero.

Binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa mutanen za su yi safarar bindigar ne ya zuwa ƙauyen Yar Galadima dake ƙaramar hukumar Maru ta jihar Zamfara.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...